Rundunar Yan Sandan Jihar Kano Ta Kama Wani Da Ya Kware Wajen Kera Bindigogi Yana Siyarwa Yan Fashi

Kakakin rundunar yan sandan jahar Kano, Magaji Musa Majiya, ya tabbatar da kama, Rabi'u Sulaiman, da ya kware wajen kera bindigogi yana sayarwa Yan fashin dake addabar jama'a a dajin falgore da titin Kano-Zaria-Kaduna.
Kakakin Yan sandan ya rubuta a shafin Sa na facebook kamar haka "
Wannan shine Rabiu Suleman Mutumin Kauyen Fadan Yalwa dake Karamar Hukumar Tudun Wada, shi kwararre ne wajen kera bindiga kala-kala yana sayarwa da Yan fashi dake addabar Jama’a a Dajin Falgore da Titin Kano-zuwa Zaria da Kaduna da sauran yankunan kudancin Kano. Mun kama shi da bindigogi da harsashi mai yawa kuma ana cigaba da gudanar da bincike".
Shiga shafin mu na Facebook

Comments

Labarum da su ka fi Jan hankalin makarantan mu

Buhari Zai Dawo Najeriya A Yau

Dalilin da yasa Hafizu Abubakar ya ajiye makamin sa na mataimaki na - Ganduje

Hafiz Abubakar ya ajiye makaminsa na mataimakin gwamnan Kano

Jahohi 21 da ake sa ran shugaba Buhari zai lashe a zaben 2019