Kwallon Da Ronaldo Ya Ci Juventus Ta Zo Ta Daya A Nahiyar Turai

Hukumar da ke gudanar da kwallo a nahiyar turai, UEFA, ta zabi kwallo ta biyu da Cristiano Ronaldo ya ci Juventus a yayin karawar su da Real Madrid a kakar wasannin da ta gabata, a matsayi na daya.

Dan Portugal din dai ya sami kyautar bayan cin watsiya da yayi a yayin wasan  da saida hakan ya burge magoya bayan Juventus din da har suka tashi tsaye suka jinjina masa akan bajintar da yayi.

Comments