Hukumar yan sanda ta jihar Ondo ta bayar da sanarwar rasuwar Wanda ake zargi da garkuwa da mutane da ta kama a garin Owo, saboda ya sha kwayar tramadol ta yi masa karo.
Shugaban kasar Najeriya, Muhammad Buhari, zai dawo gida Najeriya yau bayan ya shafe kwanaki goma da ya tafi hutun aiki a Ingila. Shugaban kasar ya tafi hutun ran 3 ga watan August, inda ya bar mataimakinsa, Yemi Osinbajo a matsayin mukaddashin shugaban kasa. Babban mai taimakawa shugaban kasar ta bangaren yada labarai, Garba Shehu, shi ya tabbatar da cewa Buhari 'zai dawo a yau' kodayake bai fadi takamaiman lokacin da zai dawo a yau din ba. Kofi Anan ya rasu kwankwaso ya hau jirgin saman daya daga cikin wadanda ya waje dan su koyi tukin Jirgi facebook din mu
Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya mai da martani akan ajiye aikin da mataimakin sa, Hafizu Abubakar, yayi. Ya bayyana cewa akwai zargi akan tsohon mataimakin nasa na kashe sama da naira miliyan dari da hamsin akan tafiye-tafiyen kasashen ketare da na cikin gida. Ganduje ya ce mataimakin nasa ya ajiye aiki ne dan gudun shirin tsige shi da talatin cikin arba'in na 'yan majalisar za su yi masa saboda zarge-zarge da kuma cin dunduniyar gwamnatin ta Kano.
Mataimakin gwamnan Kano, prof. Hafizu Abubakar, ya ba wa gwamnatin Kano takardar ajiye aikin shi yau lahadi saboda rashin jituwa tsakanin sa da gwamnan Kano. A takardar ajiye aikin tsohon mataimakin gwamnan ya bayyana cewa yana da sha'awar ci gaba da kasancewa a makamin sa har zuwa karshen wa'adin gwamnatin, amma ya zabi ya ajiye makamin nasa saboda bambancin abubuwa da ba za a iya shawo kansu ba.
Jahohi 21 da ake sa ran shugaba Buhari zai lashe a zaben 2019 Yayin da shekarar zabe ta 2019 ke ta kara matsowa, masana harkokin siyasa da ma masu fashin baki akan al’amurra na ganin cewa har yanzu fa shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ke kan gaba wajen farin jini a al’ummar kasar. Kamar yadda suka bayyana za’a iya ganewa idan aka yi duba na tsanaki a tsakanin kafatanin jahohin Najeriya aka kuma dora su akan sikelin wadanda zai iya lashewa da kuma faduwa a zaben mai zuwa. Duk da dai har yanzu jam’iyyar adawa ta PDP bata fitar da nata dan takarar ba, amma dai ana hasashen cewa shugaba Buhari zai iya lashe akalla jahohi 21 a zaben mai zuwa. Idan kuma aka hada da babban birnin tarayya, to a iya cewa ma jahohi 22. Ga dai su kamar haka: 1. Adamawa 2. Bauchi. 3. Borno 4. Ekiti 5. Gombe 6. Jigawa 7. Kaduna 8. Kano 9. Katsina 10. Kebbi 11. Kogi 12. Lagos 13. Nasarawa 14. Niger 15. Ogun 16. Ondo 17. Osun 18. Oyo 19. Sokoto 20. Taraba 21. Zamfara 22. Sai kuma babban bi
Comments