Posts

Showing posts from July, 2018

Dr. Bukola saraki ya bayyana ficewar sa daga APC

Image
 Shugaban majalisar dattijai ta Nigeria, Dr. Bukola Saraki ya bayyana ficewar sa daga jam'iyyar APC. Ya bayyana a shafin sa na twitter cewa ya yanke shawarar ficewar ne bayan tuntubar manya da yayi a kan hakan.

China ta shirya kaddamar da gada mafi tsawo a duniya

Image
China tana tsaka da muhimman ayyukan raya kasa da za su bunkasa ci gaban jihohin ta. China ta shirya dan tsugunar da yan kasar ta mutum miliyan Dari biyu da hamsin, a cikin sababbin biranen da ta ke ginawa yanzu.           Kasar ta kashe sama da naira tiriliyan dari a kokarin ta na tsugunar da yan kasar ta a cikin wadannan gagaruman ayyukan raya kasar. Gada mafi tsawo a duniyan (34 miles) da ta hada Hong Kong, Macau da Mainland China, ta kunshi gada mai siffar maciji da hanyar wuce wa a kasan Ruwa.

Cristiano Ronaldo ya hadu da abokan wasan sa na Juventus a karon farko

Image
Cristiano Ronaldo ya hadu da abokan wasan sa na juventus a karon farko, a yayin da  aka sake duba lafiyar sa a karo na biyu a asibitin kungiyar kwallon. Ronaldo, da ya rattaba wa Juventus contract na shekara hudu a kan kudi naira biliyan arba'in da hudu (£105m), ya iso Turin jiya da niyyar fara atisaye tare da abokan wasan nasa. Dan portugal din ya gaisa da Higuain tare da Dybala, wadanda zuwan sa ya zama barazana ga ci gaba da zaman su a kulob din a kaka mai kamawa. Jarumi ka iya ka huta!

Ganduje ya ce ba sa hannun sa a cikin tsige shugaban majalisar Kano

Image
Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya nesanta kansa daga cikin wadanda suka kitsa tsige shugaban majalisar jihar, Yusuf Ata. Gwamnan ya ce bai san komai ba akan shirin tsige shugaban majalisar. DAILY POST ta ruwaito cewa da safiyar litinin, 27 daga cikin 40 na yan majalisar suka sa hannu a kan takardar tsige shugaban majalisar da ke wakiltar karamar hukumar Fagge. Gwamnan  ya fadawa manema labarai a lokacin da ya karbi sabbin jagororin majalisar, da Kabiru rurum ya jagoranta a gidan gwamnati ran litinin cewa, yaji labarin tsigewar ta kiransa da akai ta yi a waya. Kwankwaso ya kai wa shekarau ziyara

Wani da ya fara aiki a kamfanin jiragen sama a matsayin mai goge-goge ya zama captain

Image
 Muhammad Abubakar ( na tsakiya) da ya fara aiki a kamfanin jirgin sama na Azman shekara ashirin da hudu da ta wuce a matsayin mai goge-goge, ya cimma burin sa na zama kwararren ma'aikacin jirgin sama, inda yanzu aka kara masa matsayi zuwa babban hafsan jirgi wato captain. Sakon twitter daga daga ainihin shafin jirgin saman na @AirAzman shi ya tabbatar da hakan. zakaran da Allah ya nufa fa cara...

Dalilin da yasa aka tsige shugaban majalisa a Kano

Image
Kamfanin jaridar Daily trust, ya gano cewa an tsige shugaban majalisar ne saboda da zargin cin hanci da rashawa. Wani zargin kuma da su ke wa tsohon shugaban majalisar ya hadar da zuwa majalisa a makare. Sun kuma tuhume shi da rashin aiki tare da manyan ofisoshin majalisar wajen gudanar da majalisar. Wasu labaran na zuwa anjima.

Adadin masu neman shugabancin kasa ya kai 46 a halin yanzu, karanta sunayen su

Image
A dai dai lokacin da ya kasance kusan kwana 200 kawai ya rage a yi zaben shugaban kasa, kamfanin jaridar daily trust sun hada adadin wadanda su ka bayyana aniyar su ta fito wa takarar shugaban kasa. Jadawalin hukumar zabe dai ya tsaida 16th February 2018, a matsayin ranar zaben shugan kasa da na yan majalisun tarayya.  • Kwankwaso ya ziyarci shekarau• Akasarin yan takarar dai suna jamaiyyar PDP, sai APC na biye mata. Wasu yan takarar ma ba su bayyana takamaimiyar jamaiyyar da za su tsaya takara ba. Masu fatan dare mafi kololuwar kujerar dai kamar yadda Haruna Ibrahim ya tattara sunan su sune: 1. Kingsley Moghalu 2. Sule Lamido- Pdp 3. Donald Duke-Pdp 4. Kabiru Tanimu Turaki-Pdp 5. Ahmed Mohammed Makarfi-Pdp 6. Ibrahim Dankwambo-Pdp 7. Muhammadu Buhari-Apc 8. Fela Durotoye- 9. Funmilayo Adesanya-Davies- Pdp 10. Remi Sonaiya- Kowa 11. Thomas-Wilson Ikubese 12. Omoyele Sowore 13. Enyinnaya Nnaemeka Nwosu 14. Ahmed Buhari 15. Peter Ayodele Fayose-Pdp 16. Adesanya F

Abu goma da ke janyo mutuwar barin jiki

Image
  Mutuwar barin jiki na faruwa ne idan kwakwalwa ta gaza samun isashshen jini a dalilin fashewa ko toshewar magudanan jini da suke ba ta jini. Duk bangaren kwakwalwa da ya kasa samun jini na tsawon minti daya yana mutuwa, sai bangaren jiki da wannan waje ke sarrafawa ya rasa aikinsa. Abubuwa goma da za su iya janyo mutuwar barin jiki da suke sanadiyyar toshewa ko fashewar mesar da ta ke ba wa kwakwalwa jini sune: 1. Hawan jini.  Shi yafi komai yawan janyo mutuwar barin jiki. Alamun hauhawar jinin tana farawa daga 140/90mmHg. 2.  Taba sigari.  Hayakin sigari yana kara kaurin jini, yana kara gudun jini sannan kuma yana sa magudanan jini suyi tauri 3.  Ciwon zuciya.  Zuciya tana iya samun tawaya tun a cikin uwa ko a yayin tsufa ko ma kitse ya toshe manyan hanyoyin jinin. 4.  Ciwon sikari.  Akasarin masu wannan ciwon suna da hawan jini. Yawan sikarin a cikin jini na janyo lalacewar magudanan jinin. 5.  Kiba da te'ba.  Kiba tana da alaka da yawan kitse a cikin jiki, wannan

Kwankwaso ya ziyarci Shekarau a Abuja

Image
Tsohon gwamnan Kano, mallam Ibrahim Shekarau ya karbi bakuncin sanatan Kano ta tsakiya wato Dr. Rabiu Musa Kwankwaso a gidan sa da ke Asokoro Abuja. Mallam Shekarau da ya yi gwamnan Kano har so biyu a jere ya tabbatar da hakan a shafin sa na Facebook. • Bani da niyyar komawa APC

Kalli Sabon hotunan Rahama Sadau tare da 'yan uwanta

Image
A jiya juma,a shararriyar yar fim din kanywood da nollywood wato Rahama Sadau ta bayyana farin cikin ta tare da haduwa da ta yi da yan uwanta shakikai.

Buhari zai tafi jihar Lome dake kasar Togo gobe lahadi

Image
Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tashi gobe zuwa Lome dake kasar Togo dan yin wadansu muhimman taruka guda biyu. Babban mai taimakawa shugaban kasa akan kafofin yada labarai, Garba Shehu, ya bayyana haka yau asabar ga manema labarai. Yace shugaban zai gana da yan Nigeria mazauna Togo da kuma ofishin jakadancin Nigeria a ran lahadin. Ya kara da cewa shugaban zai halarci taron ECOWAS ran litinin.

Buhari ya bukaci magoya bayansa da su dakatar da yakin neman zaben sa a halin yanzu

Image
A jiya asabar Shugaba Muhammad Buhari ya roki magoya bayan sa na kasa gaba daya da su dakatar da yakin neman zaben sa da su ka fara. Ya yi wannan furucin ne ta bakin mataimakin sa a kan yada labarai wato Femi Adesina inda ya kara da cewa hukumar zabe tana da jadawalin ta na harkokin siyasa, dan haka suyi hakuri lokacin ya yi. Buhari ya ce ya yaba da kaunar da suke nuna masa kuma zai tanadar da aiyukan ci gaba da za su yi amfani da su wajen nuna nasarar da gwamnati ta yi a kan ci gaban kasa.

Manchester united sun sayo Willian daga Chelsea

Image
  Chelsea ta amince ta karbi tayin €75m da Manchester united ta yi musu akan dan was an su dan kasar Brazil wato Willian. Chelsea ta ki yarda tun farko ta shiga cinikin dan wasan da kungiyar kwallon Barcelona amma kuma yanzu ta sayar wa da Manchester United dan sun fi samin daidaito a kan 'ka idoji da sharuddan da Chelsea ta gindaya wa cinikin. Daga Daga cikin sharuddan akwai bukatar Mourinho ya hada da dan bayan Chelsea wato Garry Cahill a cikin cinikin.

Wani kasurgumin dan Daba ya shiga hannun 'yan sanda a Kano

Image
Yan sanda sun cafke wani dan Daba mai suna Hafiz Magaji na unguwar tudun Murtala da ke Kano. An ce sai da ya Sassari  uku daga cikin yan bangar da su ka kama da misalin karfe biyun dare a yayin da yaje balle wani shago.

Hotuna daga bikin auren dan marigayi Umaru Musa Yar'adua

Image
Wadannan hotuna ne daga bikin Barrister Ibrahim Umar Yar'dua tare da amaryarsa Saratu sodangi. An fara walimar bikin jiya alhamis 26/07/18 a Kaduna inda suka fara da walimar dare woto dinner party Lamar yadda majiyar mu ta zenithnaija.com ta wallafa.

Tsohon gwamnan jahar Gombe Abubakar Hashidu ya rasu

Image
Tsohon Gwamnan jihar Gombe, Abubakar Hashidu Ya Rasu Shine gwamnan farar hula na farko a jihar Gombe, Abubakar Habu Hashidu ya rasu a yau Juma'a sakamakon rashin lafiya da ya jima yana fama da ita. Ya rike mukamin Gwamnan Gombe ne daga 1999 zuwa 2003 a karkashin jam'iyyar ANPP. Sannan kuma ya yi ministan ruwa a zamanin mulkin soja karkashin Janar Ibrahim Badamasi Babangida.          

Ba ni da niyyar koma wa APC – Shekarau

Image
Tsohon Gwamnan Kano kuma jigo a jam'iyyar PDP Malam Ibrahim Shekarau ya ce ba shi da niyyar komawa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya. Shekarau na mayar da martani ne kan wasu rahotanni da ke cewa Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje na zawarcinsa zuwa APC. A ranar Alhamis wasu kafafen yada labarai suka bayar da rahoton cewa jiga-jigan APC a Kano da Abuja sun fara tattaunawa da Malam Shekarau da nufin shawo kansa zuwa jam'iyyar. Jaridar Daily Trust ta ce lamarin ya karfafa ne saboda sauya shekarar da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda abokin hamayyar siyasar Shekarau ne, ya yi daga APC zuwa PDP. Sai dai mai magana da yawun tsohon gwamnan Sule Ya'u Sule, ya shaida wa BBC cewa mutanen da jaridar ta ce sun gana da APC ba wakilansu ba ne, kuma ba da yawun tsohon gwamnan suka yi ba. "Ya ce ba da hannun malam suka yi ba. Wadannan mutane ne da dama can sun raba-gari da Malam Shekarau," a cewar Sule Ya'u. Ya kara da cewa ba su da "masaniyar" g

Alamomi 16 da za su tabbatar wa namiji mace tana sonsa

Image
1. KALLO: Mata suna aika sakonni da yawa ta hanyar kallo, kamar So, raini, tsoro, ba ruwana dakai da sauransu, kuma kowane ba sai an fassarawa mutum ba da ya gani yasan me ake nufi 2. KULAWA: Wannan na nufin ta nuna ta damu dashi a kowanne lokaci, ta hanyar kokarin jin halin da yake, lafiyarsa da kuma al'amuransa. Ko yana kusa da ita ko kuma nesa da ita. Idan abun murna ya sameshi ta tayashi idan na jaje ya sameshi ta jajanta masa. Ba shakka wannan yana nuna soyayya. 3. BIYAYYA: Mace ta rinka girmama namiji, abokansa da 'yan'uwansa a duk lokacin da zata mu'amalance shi ko su, a gaisuwa ne, a magana ce, a rubutaccen sako ne duk wadannan yana bukatar yaga ladabi acikinsu kada ta rinka yi masa tsiwa da rashin kunya da sauran dabi'u da zasu nunawa mutum ba a dauke shi abakin komai ba. 4. HAKURI: Babban abinda yafi bada wahala a mu'amala kuma a kafi jarraba mutum akai shine hakuri, ya zamanto namiji ya gamsu da hakurin mace ta kowace hanya kar ta rinka yi masa kok

Kalli yadda elrufa'i ya tarbi Buhari yau a kaduna

Image
Shugaban kasa Muhammad Buhari ya je Kaduna yau dan bikin yaye sojoji inda ya samu tarba ta musamman data gwamnan jihar Nasir el rufa'i. Na samo daga:Zenithnaija.com

Kwallon da Ahmad Musa ya ci ta zo matsayi na takwas

Image
An sanya kwallon dan wasan super eagles wato Ahmad Musa a matsayi na takwas a cikin dukkanin kwallayen da aka zura a FIFA world cup da aka yi a Russia. Benjamin Parvard na France shine ya zo na daya. Ga list din: Pavard (France) vs Argentina . Quintero (Mexico) vs Japan . Modric (Croatia) vs Argentina . Ronaldo (Portugal) vs Spain . Messi (Argentina) vs Nigeria . Cheryshev (Russia) vs Croatia . Chadli (Belgium) vs Japan . Musa (Nigeria) vs Iceland . Quaresma (Portugal) vs Iran . Kroos (Germany) vs Sweden

Sunayen ragowar sanatoci 53 da su ka rage a APC

Image
Labaraiblogs ta samo sunayen sanatoci da suka rage a APC biyo bayan ficewa daga jam'iyyar da wasu sanatoci suka yi ranar Galata. Adamu Aliero(Kebbi) Yahaya Abdullahi(Kebbi) Bala Ibn Na’Allah(Kebbi) Aliyu Wammako(Sokoto) Ibrahim Gobir(Sokoto) Ahmed Yerima(Zamfara) Kabir Marafa(Zamfara) Tijjani Kaura(Zamfara) Abu Ibrahim(Katsina) Umar Kurfi(Katsina) Kabir Gaya(Kano) Barau Jibrin(Kano) Abdullahi Gumel(Jigawa) Sabo Mohammed(Jigawa) Shehu Sani(Kaduna) Ahmed Lawan(Yobe) Bukar Abba Ibrahim(Yobe) Ali Ndume(Borno) Abu Kyari(Borno) Baba Kaka Garbai(Borno) Sabi Abdullahi(Niger) David Umar(Niger) Mustapha Muhammed(Niger) Abdullahi Adamu(Nasarawa) George Akume(Benue) Joshua Dariye(Plateau) Francis Alimikhena(Edo) Andrew Uchendu(Rivers) Magnus Abe(Rivers) Ovie Omo-Agege(Delta) John Enoh(Cross River) Nelson Effiong(Akwa Ibom) Andy Uba(Anambra) Sonni Ogbuoji(Ebonyi) Hope Uzodinma(Imo) Ben Uwajimogu(Imo) Danjuma Goje(Gombe) Binta Masi Garba(Adamawa) Ahmed Abub

Wani matashi ya sha ruwan kwata akan komawar Kwankwaso PDP

Image
Duk Chikin Farin Chikin Komawar Mai Girma Jagora Sen Kwankwaso PDP Yasa Matashi Dan Gwagwarmaya Abba Alka Yasha Ruwa kasa" Source: http://mandynews.com/2018/07/25/man-drinks-muddy-water-for-senator-kwankwaso/

Fayose ya kai wa saraki ziyarar goyon baya

Image
Gwamnan jihar Ekiti mai barin gado, Ayodele Fayoshe ya bayyana gwamnatin Buhari a matsayin gwamnatin marasa Imani, biyo bayan farmaki da mamaya da jami’an Yansanda suka kai wa shugaban majalisar dattawan Najeriya da mataimakinsa a gidajensu dake Abuja. Fayose ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyara da ya kai gidan Saraki da Ekweremadu don nuna ana tare a jiya Talata, 24 ga watan Yuli, inda ya bayyana ziyarar tasa da nufin kara wa Sanatocin biyu kwarin gwiwa sakamakon tsangwamar da suke fuskanta daga hannun Yansanda. Na samo wannan labarin datahttps://mobile.facebook.com/Jaridarzinariya/photos

Dole Kwankwaso ya bi kaidojin jam' iyya - Shekarau

Tsohon gwamnan Kano mallam Ibrahim shekarau ya bayyana shigowar sanatan Kano ta tsakiya zuwa PDP wato Rabiu Kwankwaso a matsayin ci gaban jam iyyar. Sannan ya bukace shi shi da magoya bayan sa da su zama masu biyayya ga tsarin mulkin jamiyyar. Tushen labari:http://thenationonlineng.net/defection-kwankwaso-abide-rule-shekarau/