Ba ni da niyyar koma wa APC – Shekarau

Tsohon Gwamnan Kano kuma jigo a jam'iyyar PDP Malam Ibrahim Shekarau ya ce ba shi da niyyar komawa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Shekarau na mayar da martani ne kan wasu rahotanni da ke cewa Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje na zawarcinsa zuwa APC.
A ranar Alhamis wasu kafafen yada labarai suka bayar da rahoton cewa jiga-jigan APC a Kano da Abuja sun fara tattaunawa da Malam Shekarau da nufin shawo kansa zuwa jam'iyyar.
Jaridar Daily Trust ta ce lamarin ya karfafa ne saboda sauya shekarar da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda abokin hamayyar siyasar Shekarau ne, ya yi daga APC zuwa PDP.
Sai dai mai magana da yawun tsohon gwamnan Sule Ya'u Sule, ya shaida wa BBC cewa mutanen da jaridar ta ce sun gana da APC ba wakilansu ba ne, kuma ba da yawun tsohon gwamnan suka yi ba.
"Ya ce ba da hannun malam suka yi ba. Wadannan mutane ne da dama can sun raba-gari da Malam Shekarau," a cewar Sule Ya'u.
Ya kara da cewa ba su da "masaniyar" ganawar da aka ce Ganduje ya yi da wasu da ke ikirarin cewa su wakilan Shekarau ne.
Buhari ya yi wa su Kwankwaso fatan alheri
Sunayen sanatocin APC da suka koma PDP
Tun bayan da tsohon Gwamna Kwankwaso ya bayyana ficewa daga APC zuwa PDP, masana ke sanya alamar tambaya kan yadda tafiya za ta kasance tsakaninsa da Malam Shekarau.
Manyan 'yan siyasar biyu sun dade suna hamayya da juna tun shekarar 2003 lokacin da Shekarau ya kayar da Kwankwaso a zaben gwamnan jihar.
Daga bisani kuma Kwankwaso ya sake yunkurowa ya kwace mulkin bayan Shekarau ya kammala wa'adinsa a shekarar 2011.
Wata majiya mai karfi a bangaren Kwankwaso ta shaida wa BBC cewa tsaffin gwamnonin biyu na da kyakkyawar fahimta da juna a yanzu, kuma nan gaba kadan za su hadu.
Masu sharhi na ganin idan har mutanen biyu suka yi aiki tare to za su iya zama babban kalubale ga jam'iyyar APC a Kano.
 Daga bbchausa.com


Comments

Labarum da su ka fi Jan hankalin makarantan mu

Buhari Zai Dawo Najeriya A Yau

Dalilin da yasa Hafizu Abubakar ya ajiye makamin sa na mataimaki na - Ganduje

Hafiz Abubakar ya ajiye makaminsa na mataimakin gwamnan Kano

Jahohi 21 da ake sa ran shugaba Buhari zai lashe a zaben 2019