A jiya juma,a shararriyar yar fim din kanywood da nollywood wato Rahama Sadau ta bayyana farin cikin ta tare da haduwa da ta yi da yan uwanta shakikai.
Birtaniya ta dawowa da Najeriya £70m, ta yi alkawarin dawo da kari anan gaba Gabanin zuwan Firam Ministan Birtaniya nan Najeriya, gwamnatin kasar ta dawowa da Najeriya da wasu makudan kudade da wani ma’aikacin gwamnatin Najeriya ya kai kasar. Kasar Birtaniya ta dawowa Najeriya da makudan kudi £70m da aka kwato daga hannun wani barawon gwamnati da ya sace kuma wata kotun Italiya ta kama shi. Jakadan Birtaniya zuwa Najeriya, Mr Paul Arkwright, ya bayyana hakan ne yayinda yake jawabi ga manema labarai a birnin tarayya Abuja. Yace:“Akwai wata karar kotun Italiya da wani mutum, Wani kashin kudin na ajiye kasar Birtaniya kuma an maido da kudin Najeriya kwanan nan. Saboda hakane aka dawo da Fam milyan 70." Amma jakadan Mr Paul Arkwright,ya ki bayyana sunan dan Najeriyan da ya kai kudin Najeriya wajen. Ya ce dai za’a dawo da karin kudi inda ya jaddada cewa kasarsa na aiki da gwamnatin Najeriya domin kara saurin gudun yadda za’a dawo da su.
Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce babban abin da zai sa a gaba bayan komawarsa aiki daga hutu shi ne daure barayi. Muhammad Buhari ya bayyana haka ne a hirar sa da gidan talbijin na NTA jim kadan bayan ya isa fadar shugaban kasar da ke Abuja, babban birnin tarayyar kasar. Bayan da aka tambaye shi game da abin da zai sa a gaba bayan ya yi hutun kwana goma, Shugaba Buhari ya ce "za mu daure barayi da yawa wadanda suka jefa mu cikin matsin tattalin arziki. Da ma na san ana sa ran zan yi hakan, kuma zan yi." Yaki da cin hanci da rashawa na cikin manyan abubuwan da Shugaba Buhari ya yi alkawarin aiwatarwa lokacin da yake yakin neman zabe. Buhari ya dawo Nigeria Tsohon shugaban majalisar dinkin duniya ya rasu
Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya nesanta kansa daga cikin wadanda suka kitsa tsige shugaban majalisar jihar, Yusuf Ata. Gwamnan ya ce bai san komai ba akan shirin tsige shugaban majalisar. DAILY POST ta ruwaito cewa da safiyar litinin, 27 daga cikin 40 na yan majalisar suka sa hannu a kan takardar tsige shugaban majalisar da ke wakiltar karamar hukumar Fagge. Gwamnan ya fadawa manema labarai a lokacin da ya karbi sabbin jagororin majalisar, da Kabiru rurum ya jagoranta a gidan gwamnati ran litinin cewa, yaji labarin tsigewar ta kiransa da akai ta yi a waya. Kwankwaso ya kai wa shekarau ziyara
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa ( INEC) ta tsawaita wa'adin rajistar katin zabe da makonni biyu inda za a kammala shirin rajistar a karshen wannan wata na Agusta. Haka ma, Hukumar INEC ta yi wa wasu kungiyoyin jam'iyyu 23 rajista a matsayin jam'iyyun siyasa inda aka tsara mika masu satifiket a ranar Alhamis mai zuwa.
Comments